Majalisar zartaswa ta tarayya ta amince da dala miliyan 183.7, domin gudanar da tuntuba da duba ayyukan shimfida layin dogo guda uku a Najeriya.
Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a fadar shugaban kasa a karshen taron zaman majalisar na mako-mako wanda shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jagoranta.
Ya ce, ayyukan sun hada daga Fatakwal zuwa Maiduguri da Kano zuwa Maradi da kuma Abuja zuwa Warri.
Ya kuma ce, “Ma’aikatar Sufuri ta gabatar da wasu takardu guda biyu kuma na farko ya na da alaka da kwangilar ayyukan tuntuba, domin kula da ayyukan layin dogo daban-daban. Kun san muna da ayyukan titin jirgin kasa guda uku ko hudu wadanda har yanzu ba a fara aiki ba, sun hada da Fatakwal-Maiduguri, Kano-Maradi sai kuma Abuja zuwa Warri”. In ji Rotimi.