fidelitybank

Lauyoyi 19 na Atiku da na Tinubu 12 suna fafatawa a kan zabe

Date:

Ɗan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya haɗa tawagar manyan lauyoyi 19 domin ƙalubalantar sakamakon zaɓen da aka yi na ranar 25 ga watan Fabarairu.

Atiku ya yi wa lauyoyin bayani a yau Laraba a hedikwatar yaƙin neman zaɓensa a Abuja, inad ya buƙace su da su tabbatar wa da kotu dokokin da aka keta a zaɓen tare da sake ƙwato abin da ya kira ikon ‘yan Najeriya.

Tawagar na ƙarƙashin jagorancin ƙwararren lauya mai zaman kansa JK Gadzama.

Ɗantakarar ya sheda musu cewa abu ne mai muhimmancin gaske su tabbatar sun tsaya tsayin daka domin tabbatar da nasara a shari’ar ba saboda shi ba kawai da PDP, domin ma sake tabbatar da dumukuraɗiyya domin ƴan gaba.

Tarin manyan lauyoyin sun haɗa da Chief Chris Uche da Paul Usoro da Tayo Jegede da Ken Mozia da Chief Mike Ozekhome da Mahmood Magaji da Joe Abraham da Chukwuma Umeh da Garba Tetengi da kuma Chief Emeka Etiaba.

Akwai kuma Chief Goddy Uche da Farfesa Maxwell Gidado da mai bayar da shawara kan shari’a na na ƙasa na PDP A.K. Ajibade da O.M. Atoyebi da Nella Rabana da Paul Ogbole da Nuremi Jimoh da kuma Abdul Ibrahim.

www.najnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp