Ɗan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya haɗa tawagar manyan lauyoyi 19 domin ƙalubalantar sakamakon zaɓen da aka yi na ranar 25 ga watan Fabarairu.
Atiku ya yi wa lauyoyin bayani a yau Laraba a hedikwatar yaƙin neman zaɓensa a Abuja, inad ya buƙace su da su tabbatar wa da kotu dokokin da aka keta a zaɓen tare da sake ƙwato abin da ya kira ikon ‘yan Najeriya.
Tawagar na ƙarƙashin jagorancin ƙwararren lauya mai zaman kansa JK Gadzama.
Ɗantakarar ya sheda musu cewa abu ne mai muhimmancin gaske su tabbatar sun tsaya tsayin daka domin tabbatar da nasara a shari’ar ba saboda shi ba kawai da PDP, domin ma sake tabbatar da dumukuraɗiyya domin ƴan gaba.
Tarin manyan lauyoyin sun haɗa da Chief Chris Uche da Paul Usoro da Tayo Jegede da Ken Mozia da Chief Mike Ozekhome da Mahmood Magaji da Joe Abraham da Chukwuma Umeh da Garba Tetengi da kuma Chief Emeka Etiaba.
Akwai kuma Chief Goddy Uche da Farfesa Maxwell Gidado da mai bayar da shawara kan shari’a na na ƙasa na PDP A.K. Ajibade da O.M. Atoyebi da Nella Rabana da Paul Ogbole da Nuremi Jimoh da kuma Abdul Ibrahim.