Shugabannin ƙasashen Larabawa za su gudanar da wani taron gaggawa a birnin Alkahira domin gabatar da shirinsu na sake gina Gaza.
Suna dai fuskantar matsin lamba a kan su fito da wani tsarin da ya bambanta da shawarar da shugaba Trump ya bayar na karɓe yankin tare da sauyawa al’ummar Falasɗinawa matsuguni.
Majiyoyin diflomasiyya da su ka ga kudurin da Masar za ta gabatar sun ce ya ba da shawarar kafa wani kwamitin wucin gadi da zai tafiyar da al’amuran Gaza da zarar an kawo karshen yaƙin Isra’ila da Hamas.
Kudurin dai bai kunshi cikakkun bayanai kan batutuwa masu sarƙaƙiya ba da suka haɗa da wanda zai biya kuɗin sake gina yankin.