Dubban mutane ne suka taru a birnin Bagadaza don nuna goyon baya ga Falasdinawan Gaza.
“Wannan gangamin na da nufin yin alla-wadai ne da abin da ke faruwa a yankin Falasdin da ke karkashin mamaya, irin zubar da jinin da ake yi da keta hakkokin dan’adam,” Abu Kayan, daya daga cikin masu shirya zanga-zangar ya fada wa kamfanin dillancin labarai na AFP.
Wannan daya ce kawai a cikin zanga-zanga da dama da aka shirya gudanarwa yau a fadin Gabas ta Tsakiya, bayan shugabannin Hamas da na Hezbollah sun yi kira ga jama’a su gudanar da zanga-zanga bayan Sallar Juma’a.
Tsohon jagoran Hamas, Khaled Meshaal a jiya ya bukaci mutane su “fita zuwa dandali da filayen Allah a fadin kasashen Larabawa da na Musulmi” don gudanar da gangami.
Ana tsammanin irin wadannan taruka da yawa za su gudana a Lebanon da Tunisia da kuma Jordan a yau.
Dakarun tsaro sun kuma shirya don tunkarar yamutsi a Masallacin al-Aqsa da ke cikin yankin mamaya a Gabashin Kudus.