Shugaban yaki da wariyar launin fata na Afirka ta Kudu, Archbishop Desmond Tutu ya mutu ya na da shekaru 90.
Tutu wanda ya lashe kyautar zaman lafiya ta Nobel wanda ya yi fice a cikin gwagwarmayar da ta kai ga kawo karshen mulkin wariyar launin fata a Afirka ta Kudu, ya kai shekaru 90.
Ya rasu ne da sanyin safiyar Lahadin nan, kuma tuni shugabannin kasashen duniya ke ci gaba da nuna alhinin su bisa irin gudunmawar da ya bayar wajen fafutukar ‘yantar da Afirka ta Kudu daga mamayar Turawan mulkin mallaka.
A cikin karramawar tasa, shugaban kasar Afrika ta Kudu, Cyril Ramaphosa, ya ce, mutuwar Tutu ta kasance “wani babi na bakin ciki a cikin bankwana da al’ummar mu ga tsararrun ‘yan Afirka ta Kudu”.
Ya kara da cewa marigayin “Fitaccen shugaba ne, mai fafutukar yaki da wariyar launin fata kuma mai fafutukar kare hakkin bil’adama a duniya”.
Ya ci gaba da bayyana shi a matsayin “Mai kishin kasa; shugaban ka’ida da Æ™wararru wanda ya ba da ma’ana ga fahimtar Littafi Mai Tsarki cewa bangaskiya ba tare da ayyuka matacce ba ne.
“Mutumin mai hankali mai mutunci da nasara a kan dakarun wariyar launin fata, ya kasance mai tausayi da rauni a cikin tausayi ga wadanda su ka fuskanci zalunci, rashin adalci da tashin hankali a karkashin mulkin wariyar launin fata, da zalunci a duniya.” A cewar Ramaphosa
Daya daga cikin fitattun shugaban Afirka ta Kudu a duniya, Tutu ya samu kyautar Nobel a shekarar 1984 saboda rawar da ya taka a gwagwarmayar kawo karshen tsarin wariyar launin fata.