fidelitybank

Lalacewar jirgin sama ya hana Shettima ya je taron ƙasashen rainon Ingila

Date:

Mataimakin Shugaban ƙasa, Kashim Shettima, ya fasa zuwa taron ƙungiyar ƙasashen renon Ingila ta Commonwealth na 2024 da za a gudanar a tsibirin Samoa, bayan da jirginsa ya samu a matsala a lokacin da ya yada zango a Amurka.

Cikin wata sanarwa da kakakin shugaban ƙasar, Bayo Onanuga ya fitar ya ce a lokacin da jirgin ya yada zango a birnin New York na Amurka, wani abu daga waje ya daki jirgin wanda kuma ya lalata gilas ɗin direban jirgin.

Sanarwar ta ce tuni shugaban ƙasar Bola Tinubu ya amince da shirya wata tawagar ministoci, ƙarƙashin jagorancin ministan muhalli, Balarabe Abbas Lawal domin wakiltar Najeriya a taron, yayin da ake ci gaba da gyaran jirgin mataimakin nasa.

An dai fara taron ne ranar 21 ga watan Oktoba, wanda kuma ake sa ran kammala shi ranar 26 ga watan Oktoba a tsibirin da ke tekun Pacific.

Sanarwar ta ce mataimakin shugaban ƙasar Kashim Shettima tare da tawagarsa da ta ƙunshi ministan harkokin waje, Yusuf Maitama Tuggar sun kama hanyar komawa Najeriya daga Amurka.

nigeria news today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp