fidelitybank

Lakuraws sun kashe Mutane 10 a Kebbi

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton ‘yan ta’addan Lakurawa ne, sun kaddamar da hare-haren hadin gwiwa a wasu kauyuka biyar na karamar hukumar Arewa ta jihar Kebbi, inda suka kashe akalla mutane 10 tare da jikkata wasu da dama.

Zagazola Makama, kwararre kan yaki da tada kayar baya da ya mayar da hankali kan yankin tafkin Chadi, ya bayyana hakan a ranar Litinin a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X.

Makama ya ce majiyoyin leken asiri sun sanar da shi cewa kauyukan da lamarin ya shafa sun hada da Birnin Debi, Garin Nagoro, da Yar Goru, da Dan Marke, da Tambo.

A cewar rahoton, ‘yan ta’addan sun far wa kauyukan ne da misalin karfe 8:48 na dare. a ranar 9 ga Maris, 2025, inda suka kona gidaje da harbe-harbe ba gaira ba dalili.

Daga cikin wadanda suka mutu har da Garba Maigari (50), yayin da sauran tara da aka kashe har yanzu ba a san ko su waye ba.

“An kai wasu da dama da suka jikkata zuwa Cibiyar Kiwon Lafiya ta Tarayya da ke Birnin Kebbi domin yi musu magani, yayin da aka ajiye gawarwakin wadanda suka mutu domin a tantance su.

“A mayar da martani, an tura sojojin Najeriya, ‘yan sanda da kuma ‘yan banga zuwa yankunan da abin ya shafa, kuma an ce an dawo da zaman lafiya,” in ji Makama.

daily 
post news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...
X whatsapp