Wasu mahara da ake zargin mayaƙan ƙungiyar Lakurawa ne sun kai hari a garin Natisini a karamar hukumar Argungu da ke jihar Kebbi.
Bayanan da BBC ta tattara sun nuna cewa maharan ɗauke da makamai sun kashe akalla mutum uku, biyu daga cikinsu jami’an tsaro na ‘yansanda, a harin na ranar Alhamis da dare.
Kazalika, sun sace shanu da dama, wanda ya jawo mutanen garin da dama suka tsere zuwa wasu wurare na daban.
Wasu mazauna garin sun shaida wa BBC cewa da misalin ƙarfe 10:00 na dare suka fara harbe-harbe.
Shugaban ƙaramar hukumar Argungu, Aliyu Sani Gulma, ya faɗa wa manema labarai ta wayar tarho cewa shanun da maharan suka sace sun kai aƙalla 200.
Mai magana da yawun rundunar ‘yansandan Kebbi, ASP Nasiru Abubakar, ya tabbatar wa BBC faruwar lamarin amma bai yi ƙarin bayani ba saboda yana kan hanyar zuwa wurin da abin ya faru a lokacin.