fidelitybank

Lakurawa sun kashe Mutane 15 a Sokoto

Date:

Wasu da ake zargin mambobin ƙungiyar Lakurawa ne sun kashe mutum 15 a wani mummunan hari da suka kai ƙauyen Kwalajiya da ke ƙaramar hukumar Tangaza a jihar Sokoto.

Harin ya faru ne da misalin ƙarfe 2:00 na rana a ranar Talata.

Ana zargin harin martani ne bayan kashe wasu mutum uku daga cikin kungiyar, ciki har da wanda ake zargin shugabansu ne a wani harin da ya ci tura da suka kai a baya a garin.

Ɗaya daga cikin shugaba a yakin da ya nemi a ɓoye sunansa ya shaidawa jaridar Daily Trust cewa maharan sun dira ƙauyen ne a daidai lokacin da jama’a ke cikin masallaci suna sallar Azahar.

“Muna cikin masallaci lokacin da suka kawo hari da yawansu.

“Da zuwansu suka fara harbe-harbe.” inji shi.

Ya ƙara da cewa jami’an tsaro da shugaban ƙaramar hukumar sun ziyarci ƙauyen a ranar Laraba don halartar jana’izar waɗanda aka kashe.

“Wannan shi ne karo na farko da ƴan Lakurawa suka kai hari kai tsaye a garinmu.

“Amma ina ganin martani ne bayan kashe wasu daga cikin su a wani harin da ya faru a baya,” inji shi.

Wani mazaunin yankin da lamarin ya shafa ya ce maharan sun ƙone gonaki da gidaje da dama tare da lalata wata ariya ta sadarwa.

tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp