fidelitybank

Laifin Tinubu ne tsadar rayuwar da Arewa ke fama da ita – Dan Bilki Kwamanda

Date:

Wani fitaccen mai sukar siyasa a Kano, Abdulmajid Danbilki Kwamanda, ya zargi Shugaba Bola Ahmed Tinubu da yin watsi da Arewa, yana mai cewa manufofinsa sun kara tabarbarewar tattalin arziki a yankin.

A cikin wani faifan bidiyo na TikTok, Danbilki, wanda fitaccen jigo ne a jam’iyyar APC, kuma mai goyon bayan tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya caccaki gwamnatin Tinubu kan yadda take tafiyar da tattalin arziki, musamman tsadar rayuwa.

Ya yi nuni da cewa, farashin kayan masarufi ya yi tashin gwauron zabo, inda ya ce buhun shinkafa da ya kai Naira 26,000 a zamanin mulkin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, yanzu ana sayar da shi kan Naira 96,000.

Danbilki ya bukaci Tinubu da ya gaggauta tunkarar wadannan kalubalen tattalin arziki kafin zaben 2027, yana mai gargadin cewa tabarbarewar yanayi na iya zubar da amanar jama’a.

Ya kuma caccaki ‘yan siyasar Arewa a gwamnatin Tinubu, inda ya zarge su da fifita bukatun kashin kai fiye da ci gaban yankin.

A cewarsa, duk da kasancewarsu a cikin harkokin gwamnati, sun kasa bayar da shawarwarin manufofin da za su amfani Arewa.

Da yake tunatar da su cewa mulki na wucin gadi ne, ya yi kira ga wadannan jami’an da su ingiza ci gaba mai ma’ana kafin wa’adinsu ya kare.

sani ahmad

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban Ĉ™aramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen Ĉ™asa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi Ĉ™orafe-Ĉ™orafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...
X whatsapp