Wani fitaccen mai sukar siyasa a Kano, Abdulmajid Danbilki Kwamanda, ya zargi Shugaba Bola Ahmed Tinubu da yin watsi da Arewa, yana mai cewa manufofinsa sun kara tabarbarewar tattalin arziki a yankin.
A cikin wani faifan bidiyo na TikTok, Danbilki, wanda fitaccen jigo ne a jamâiyyar APC, kuma mai goyon bayan tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya caccaki gwamnatin Tinubu kan yadda take tafiyar da tattalin arziki, musamman tsadar rayuwa.
Ya yi nuni da cewa, farashin kayan masarufi ya yi tashin gwauron zabo, inda ya ce buhun shinkafa da ya kai Naira 26,000 a zamanin mulkin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, yanzu ana sayar da shi kan Naira 96,000.
Danbilki ya bukaci Tinubu da ya gaggauta tunkarar wadannan kalubalen tattalin arziki kafin zaben 2027, yana mai gargadin cewa tabarbarewar yanayi na iya zubar da amanar jamaâa.
Ya kuma caccaki âyan siyasar Arewa a gwamnatin Tinubu, inda ya zarge su da fifita bukatun kashin kai fiye da ci gaban yankin.
A cewarsa, duk da kasancewarsu a cikin harkokin gwamnati, sun kasa bayar da shawarwarin manufofin da za su amfani Arewa.
Da yake tunatar da su cewa mulki na wucin gadi ne, ya yi kira ga wadannan jamiâan da su ingiza ci gaba mai maâana kafin waâadinsu ya kare.