Kungiyar gwamnonin jihohi ta ƙasa, ta ce, ikirarin da gwamnatin tarayya ta yi a kan cewa, gwamnonin jihohin kasar su ne suke da alhakin karuwar talauci a kasar, magana ce da ba ta da tushe ballantana makama.
Kungiyar ta NGF ta mayar da martani ne kan kalaman da karamin ministan kudi na kasar Clem Agba ya yi a baya-bayam nan inda ya zargi gwamnonin da rashin daukar matakan inganta rayuwar mazauna karkara.
A maimakon haka ya ce, sun fi ba ayyukan samar da ababan more rayuwa a birane fifiko da yin gine-gine.
A cewar ministan kudin kashi 72 cikin 100 na al’ummar kasar da ke fama kangin talauci na zaune ne a yankunan karkara inda ya yi ikirarin cewa gwamnoni sun yi watsi da su.
Sai dai Abdul Razak Bello Barkindo wanda shi ne kakakin kungiyar gwamnonin ta Najeriya ya shaida wa BBC cewa kalaman ministan ya bai wa gwamnonin kasar mamaki.
“ Ba mu zaci cewa shi wannan ministan zai yi furuci irin wannan ba, dalili kuwa shi ne ba mu saba ka-ce-na-ce da gwamnatin tarayya ba, sannan kuma bai cancanta ba, saboda gwamnatin tarayya tana da gwamnoni 22 a cikin jam’iyyarta.’’ In ji shi.
Ya kara da cewa, ‘’Idan gwamnatin tarayya tana ganin akwai abin da ya kasa toh ina ganin irin manufofin jam’iyyar ce ta kasa., ba su hana su yi abin da ya kamata su yi ba.’’