fidelitybank

Laifin gwamnatin Buhari ne sanadin talauci a ƙasa – Ƙungiyar Gwamnoni

Date:

Kungiyar gwamnonin jihohi ta ƙasa, ta ce, ikirarin da gwamnatin tarayya ta yi a kan cewa, gwamnonin jihohin kasar su ne suke da alhakin karuwar talauci a kasar,  magana ce da ba ta da tushe ballantana makama.

 Kungiyar ta NGF  ta mayar da martani ne kan  kalaman da karamin ministan kudi na kasar Clem Agba ya yi a baya-bayam nan inda  ya zargi gwamnonin  da rashin  daukar matakan inganta rayuwar mazauna karkara.

A maimakon haka ya ce, sun fi ba ayyukan samar da ababan more rayuwa a birane fifiko da yin gine-gine.

 A cewar ministan  kudin  kashi 72 cikin 100  na al’ummar kasar da ke fama kangin talauci na zaune ne a yankunan karkara inda ya yi ikirarin cewa gwamnoni sun yi watsi da su.

Sai dai  Abdul Razak Bello Barkindo wanda shi ne kakakin  kungiyar gwamnonin ta Najeriya ya shaida wa BBC cewa kalaman ministan ya bai wa gwamnonin kasar mamaki.

“ Ba mu zaci cewa shi wannan ministan zai yi furuci irin wannan  ba, dalili kuwa shi ne  ba mu saba ka-ce-na-ce da gwamnatin tarayya ba, sannan kuma bai cancanta ba, saboda gwamnatin tarayya tana da gwamnoni 22 a cikin jam’iyyarta.’’ In ji shi.

Ya kara da cewa, ‘’Idan gwamnatin tarayya tana ganin akwai  abin da ya kasa toh ina ganin irin manufofin jam’iyyar ce  ta kasa., ba su hana su yi abin da ya kamata su yi ba.’’

www nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp