Ministan yada labarai da al’adu, Lai Mohammed, ya maka mawallafi da editan Pointblank News a babban kotu da Abuja.
Lauyoyi su na tuhumar Johnson Ude da Uduma Mba da kokarin batawa Ministan suna.
Kamfanin dillacin labarai na kasa NAN, ta rawaito cewa, takardar karar da Alhaji Lai Mohammed ya shigar a kotu, ya na zargin an yi masa kage.
Ministan na tuhumar gidan jaridar da kitsa masa karya domin, su bata masa suna, domin haka ya nemi su biya tarar Naira biliyan 50, saboda ya rage zafi.