Ministan yada labarai da al’adu, Lai Mohammed, ya yi watsi da ikirarin cewa ya kamu da cutar COVID-19.
A cikin rahotannin na baya-bayan nan ya bayyana cewa wasu hadiman shugaban kasa sun kamu da cutar, ciki harda ministan wanda ya bayyana cewa bai killace kansa ba, kuma bai kamu da cutar ba.
Gidan talabijin na Channels ta rawaito cewa, mai magana da yawun sa, Segun Aeyemi, a cikin wata sanarwa da ya fitar ya ce,”A bisa ga bayanan, ministar bai kamu da COVID-19, domin haka bai kuma kebe kansa ba”.
“Wannan rahoton, wanda wata jarida ta shafin internet ta wallafa fara wallafawa, sannan wasu manyan kafafen yada labarai sun wallafa, ya sake bayyana babban aikin da mu ke fuskanta a yakinmu na kawar da labaran karya da kuma bayanan karya. A cewar Sanarwar.