Rundunar ‘yan sandan jihar Edo, ta musanta rahotannin da ke cewa, an yi garkuwa da ɗalibai 50 da za su yi jarrabawar shiga manyan makarantu a Benin.
Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar, SP Bello Kontongs, ya bayyana rahoton a matsayin karya da yaudara.
Ya bukaci ‘yan Najeriya da su yi watsi da rahoton, inda ya kara da cewa, yana iya haifar da firgici.
Ya ci gaba da cewa, “An sanar da rundunar ‘yan sandan jihar Edo kan wani rahoto na bata-gari da aka yi ta yaɗa wa a shafukan sada zumunta, inda ake zargin wasu makiyaya sun yi garkuwa da wasu dalibai sama da 50 da ke kan hanyarsu ta zuwa rubuta UTME a Okada, Ovia North-East, kuma hakan ya haifar da rudani. a cikin jihar.