fidelitybank

Labarin mu na kaiwa Ƴan Bindiga abinci ƙarya ne – Ƴansanda

Date:

Rundunar ƴansandan Najeriya ta musanta rahotannin da ake yaɗawa cewa jirgin sama mai saukar ungulu mallakinta yana kai wa ƴanbindiga abinci a dajin jihar Kogi.

Rundunar ta ce labarin ƙanzon kurege ne da baya da tushe bare makama.

Kakakin rundunar, ACP Olumuyiwa Adejobi, ya ce bidiyon da ake yaɗawa a kafafen sada zumunta na wani aiki ne da jami’an rundunar suka yi a yankin Obajana na jihar Kogi, kuma an cika duk wata ƙa’ida kafin ƙaddamar da aikin.

Sanarwar da ACP Adejobi ya fitar ta ce “Ba kamar yadda ake yaɗa labarin ƙanzon kurege ba cewa jirgin saman mu yana kai wa ƴanbindiga abinci a cikin daji, bidiyon na wani aikin haɗin gwiwa ne tsakanin ƴansanda da ƴanbanga da mafarauta.”

Rundunar ta ce ta gudanar da aikin ne a ranar Asabar 10 ga watan Mayun 2025 a jihar Kogi.

Ta kuma yi bayanin cewa an shigar da jirgin sama mai saukar ungulun ne a cikin aikin domin tallafawa jami’an rundunar da takwarorin su a aikin su na fatattakar ƴanbindiga.

Rundunar ƴansandan Najeriyan ta yi Allah wadai da masu yaɗa wannan labaran ƙanzon kurege, tare da jaddada aniyarta ta ci gaba da gudanar da aikin ta a cikin ƙwarewa da bin doka.

legit.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...
X whatsapp