fidelitybank

Labarin mu na kaiwa Ƴan Bindiga abinci ƙarya ne – Ƴansanda

Date:

Rundunar ƴansandan Najeriya ta musanta rahotannin da ake yaɗawa cewa jirgin sama mai saukar ungulu mallakinta yana kai wa ƴanbindiga abinci a dajin jihar Kogi.

Rundunar ta ce labarin ƙanzon kurege ne da baya da tushe bare makama.

Kakakin rundunar, ACP Olumuyiwa Adejobi, ya ce bidiyon da ake yaɗawa a kafafen sada zumunta na wani aiki ne da jami’an rundunar suka yi a yankin Obajana na jihar Kogi, kuma an cika duk wata ƙa’ida kafin ƙaddamar da aikin.

Sanarwar da ACP Adejobi ya fitar ta ce “Ba kamar yadda ake yaɗa labarin ƙanzon kurege ba cewa jirgin saman mu yana kai wa ƴanbindiga abinci a cikin daji, bidiyon na wani aikin haɗin gwiwa ne tsakanin ƴansanda da ƴanbanga da mafarauta.”

Rundunar ta ce ta gudanar da aikin ne a ranar Asabar 10 ga watan Mayun 2025 a jihar Kogi.

Ta kuma yi bayanin cewa an shigar da jirgin sama mai saukar ungulun ne a cikin aikin domin tallafawa jami’an rundunar da takwarorin su a aikin su na fatattakar ƴanbindiga.

Rundunar ƴansandan Najeriyan ta yi Allah wadai da masu yaɗa wannan labaran ƙanzon kurege, tare da jaddada aniyarta ta ci gaba da gudanar da aikin ta a cikin ƙwarewa da bin doka.

legits news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp