Rundunar ƴansandan Najeriya ta musanta rahotannin da ake yaɗawa cewa jirgin sama mai saukar ungulu mallakinta yana kai wa ƴanbindiga abinci a dajin jihar Kogi.
Rundunar ta ce labarin ƙanzon kurege ne da baya da tushe bare makama.
Kakakin rundunar, ACP Olumuyiwa Adejobi, ya ce bidiyon da ake yaɗawa a kafafen sada zumunta na wani aiki ne da jami’an rundunar suka yi a yankin Obajana na jihar Kogi, kuma an cika duk wata ƙa’ida kafin ƙaddamar da aikin.
Sanarwar da ACP Adejobi ya fitar ta ce “Ba kamar yadda ake yaɗa labarin ƙanzon kurege ba cewa jirgin saman mu yana kai wa ƴanbindiga abinci a cikin daji, bidiyon na wani aikin haɗin gwiwa ne tsakanin ƴansanda da ƴanbanga da mafarauta.”
Rundunar ta ce ta gudanar da aikin ne a ranar Asabar 10 ga watan Mayun 2025 a jihar Kogi.
Ta kuma yi bayanin cewa an shigar da jirgin sama mai saukar ungulun ne a cikin aikin domin tallafawa jami’an rundunar da takwarorin su a aikin su na fatattakar ƴanbindiga.
Rundunar ƴansandan Najeriyan ta yi Allah wadai da masu yaɗa wannan labaran ƙanzon kurege, tare da jaddada aniyarta ta ci gaba da gudanar da aikin ta a cikin ƙwarewa da bin doka.