fidelitybank

Kwatsam ta ɗage sayar da shinkafarta bayan an rasa rai a wajen saye

Date:

Hukumar hana fasakwauri ta Najeriya, ta dakatar da sayar da kayan abinci da ta fara sayarwa a kan farashi mai rahusa, sakamakon turmutsitsin da ya yi sanadin salwantar rayuka a hedikwatarta da ke unguwar Yaba a birnin Legas a ranar Juma’ar da ta gabata.

Kakakin hukumar ta Kwastam Abdullahi Maiwada ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin.

A ranar 20 ga Fabrairu, 2024 ne Hukumar ta ce za ta sayar da kayan abincin da aka kama a farashi mai rahusa, domin rage wahalhalu da tsadar rayuwa a kasar.

“An fara sayar da kayan abincin a farashi mai rahusa a natse kuma cikin kamala da misalin karfe 0800,” in ji Maiwada

“Mun ji daɗin haɗin kan ɗimbin jama’a da suka haɗa da tsofaffi da nakasassu da mata masu juna biyu, da sauran ’yan Najeriya masu rauni”, inda ya kara da cewa “sayar da kayan abincin ya kasance har zuwa kusan ƙarfe 5 na yamma, kamar yadda sama da masu cin gajiyar 5000 da ‘yan jarida suka tabbatar.”

Sanarwar ta kuma kara da cewa duk da haka, rikici da tashin hankali da ba a taɓa zata ba ya ɓarke a lokacin da muka ce mun rufe sayar da kayan abinci a ranar da cewa za mu ci gaba washegari, wanda ya haifar da sakamako mara daɗi.

“Dandazon mutanen sun kasance cikin zaƙuwa inda suka riƙa ture shingayen da muka gindaya domin neman buhunhunan shinkafa wanda aka samu asarar rayuka da jikkata wasu da dama.” In ji Maiwada.

Hukumar dai ta mika ta’aziyyarta ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu a wannan mummunan lamari.

breaking news in nigeria today punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp