fidelitybank

Kwastam ta yi hadin gwiwa da tarayyar Turai kan shigo da kaya

Date:

Hukumar Kwastam ta Najeriya, NCS, ta ce tana hada kai da Darakta-Janar, na Hukumar Kula da Haraji da Kwastam, DG TAXUD, na Tarayyar Turai, EU, don inganta kasuwanci, sa ido kan fitar da kayayyaki da takardu a Najeriya.

Babban Kwanturolan Hukumar Kwastam, Adewale Adeniyi, ya bayyana haka bayan wata ganawa da Shugaban Hukumar TAXUD a ranar Talata a Abuja.

A cewarsa, haɗin gwiwar ya dace, la’akari da cewa NCS na neman sahihiyar dandamali na dijital wanda zai inganta ingancinta na takardu.

Ya kuma bayyana kwarin gwiwar cewa shirin zai bude wata sabuwar hanyar samun damammaki a tsakanin bangarorin tattalin arzikin kasashen biyu na masu rijistar fitar da kayayyaki zuwa ketare.

Ya jaddada bukatar samar da tsari tsakanin kwastam da DG TAXUD da za a yi amfani da su wajen tantancewa da tabbatar da kayayyakin da ake fitarwa zuwa kasashen waje.

“A wani bangare na shirin mu na wayar da kan jama’a, muna kuma aiki tare da sauran hukumomin gwamnatin Najeriya domin mu inganta wadannan damammaki.

“A baya, an dawo mana da kayayyaki daga Najeriya saboda inganci da kuma ajiya.

“Mun matsa don kafa wurin fitar da kayayyaki ‘daya-daya’ domin fitar da takardun fitar da kayayyaki zuwa kasashen waje, ta yadda hakan zai taimaka mana wajen rage lokacin da masu fitar da kayayyaki daga Najeriya ke dauka don fitar da kayansu daga tasharmu.

“A farkon wannan watan, mun kaddamar da nazarin sakin lokaci, wanda muke nufi don shigo da kaya da kuma nawa ne ‘yan kasuwa ke É—auka don kwashe kayansu a tashar jiragen ruwa,” in ji shi.

sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp