Hukumar hana fasa-kwauri ta Kwastam, ta ce, ta kama wasu tsuntsaye nau’in aku da shaho wadanda ke cikin kasadar bacewa daga doron duniya a lokacin da ake yunkurin fitar da su zuwa kasashen waje.
Kwanturolan hukumar na shiyyar iyakar Seme, Timi Bomodi ya sanar a ranar Litinin cewa jami’ansa sun kama tsuntsayen ne da sanyin safiyar ranar, bayan sun samu bayanan sirri, inda suka tarbe masu fasa-kwaurin a shingen bincike na Gbaji suna yunkurin shiga Jamhuriyar Benin.
Ya ce sun samu bayanan sirri cewa an kwaso tsuntsayen ne a babbar motar safa daga Kaduna zuwa Lagos, da niyyar kai su kasashen waje don sayarwa.
“Kamar yadda mai yiwuwa kuka sani, wannan haramtaccen kasuwanci na tsuntsayen da ke kokarin bacewa daga doron kasa.” Kwanturolan hukumar ya ce sun kama mutum biyu masu alaka da fasa-kwaurin tsuntsayen.