fidelitybank

Kwastam ta kama Shinkafa mai ɗauke da guba ƴar Indiya

Date:

Hukumar Kwastam a Ikeja, a ranar Alhamis, ta ce, ta kama buhunan shinkafa ‘yar waje mai guba da aka shigo da su daga kasar Indiya, aka kuma yi safarar su ta Jamhuriyar Benin zuwa cikin kasar.

Da yake jawabi yayin ganawa da manema labarai a Legas, mukaddashin Kwanturola na FOU, shiyyar A, Hussein Ejibunu, ya ce, hukumar kula da ingancin magunguna ta kasa (NAFDAC) ta yi gwajin shinkafar kasar waje, inda ta tabbatar da cewa, shinkafar na dauke da dalma (a). soft heavy toxic malleable metallic element), wanda ke da guba ga lafiyar jama’a, ko da yake ya ce, an kama mutane 12 da ake zargi da hannu wajen kame daban-daban.

Bayan mun kama shinkafar da aka yi fasakwaurin ne, sai muka kira hukumar NAFDAC, domin gudanar da binciken dakin gwaje-gwaje, an tattaro cewa, shinkafar mai suna SIMBA ta kunshi sinadarin gubar. Abun da ya kunsa yana da guba ga jiki kuma yana da hadari ga lafiyar jama’a”, in ji shi.

Ejibunu ya kuma ce, rundunar ta kama PMS lita 55,800, bale 73 na rigunan da aka yi amfani da su, firji guda 82, na’urar kwampressor guda 104, bales na sabbin masaku 143, tayoyin da aka yi amfani da su guda 1,264, katan 156 na daskararrun kaji guda 7,960. sababbin takalma da sauransu.

Ya yi bayanin cewa, bisa tsarin gwamnatin tarayya na karfafa noman shinkafa a cikin gida a kan shigo da shinkafar da ake shigowa da su waje, hukumar ta Kwastam, ta kama buhunan shinkafa 7,259 (na kilo 50 kowanne) wanda kwatankwacin manyan motoci sama da goma sha biyu (12) ne. .

natforce latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290 ya cika

A ranar Litinin ne wa'adin da wata kotu ta...

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla Ɗanbokolo ubangidan Turji

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya...

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki...

An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...

Tawagar Gwamnatin Kano ta shilla Saudiyya zuwa jana’izar Dantata

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci...

Tawagar Jami’an gwamnati da Malamai sun tafi jana’izar Dantata

Wata tawaga daga gwamnatin Tarayya, ta isa ƙasar Saudiyya...

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa...

Gwamnan Kano ya sauya wa hukumar Wasanni suna

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya sauya wa...

Dalilin da ya sa Wake ya karye a Najeriya – Ƙungiyar Manoma

Ƙungiyar manoman wake a kasar nan, ta bayyana amfani...

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...
X whatsapp