fidelitybank

Kwastam ta kama mota ɗauke da sinadaran haɗa bam

Date:

Hukumar Kwastam ta kasa, reshen yankin Seme, ta kama wata mota da ake zargin tana ɗauke da kayan haɗa bam (IED).

Wannan na ƙunshe ne a wani bidiyo da hukumar ta wallafa a shafinta na X, inda jami’anta ke binciken motar da aka kama a kan titin Lagos zuwa Badagry.

An gano cikin motar akwai kwanso guda shida na ma’adani mai launin azurfa mai ɗauke da guba mai ƙarfi da aka fi sani da corrosive mercury — wanda ake kyautata zaton ana amfani da shi wajen haɗa abubuwan fashewa.

Shugaban Kwastam na yankin, Kwanturola Ben Oramalugu, ya ce an kama mutum ɗaya da ake zargin yana da alaƙa da motar.

Ya bayyana cewa nasarar kama motar na nuna yadda Kwastam ke cikin shiri da kulawa wajen kare tsaron kasa.

Oramalugu ya kara da cewa wannan aiki na cikin matakan da Kwastam ke dauka don dakile ayyukan fasa-kwauri da sauran laifuka a iyakokin Najeriya.

Baya ga motar da ake zargin tana ɗauke da kayan haɗa bam, hukumar ta kuma kama wasu kayayyaki da dama da suka saɓa wa doka.

Kayayyakin sun hada da kuɗaɗen ƙasashen waje daga Birtaniya da Kanada, da Amurka da darajarsu ta kai kusan naira miliyan tara, wanda hakan ya saɓa dokar harajin kaya na waje.

Sauran kayayyakin da aka kama sun hada da robar ganyen wiwi guda 553 da buhunan shinkafar waje 1,415 da jarkokin man fetur guda 750, da kuma magungunan da ba a yi rijistarsu ba.

Kwanturola Oramalugu ya ce hukumar za ta miƙa kayayyakin da aka kama ga hukumomin da suka dace domin gudanar da bincike tare da ɗaukar mataki, da gurfanar da wadanda ake zargi.

latest nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp