fidelitybank

Kwastam ta kama mota ɗauke da sinadaran haɗa bam

Date:

Hukumar Kwastam ta kasa, reshen yankin Seme, ta kama wata mota da ake zargin tana ɗauke da kayan haɗa bam (IED).

Wannan na ƙunshe ne a wani bidiyo da hukumar ta wallafa a shafinta na X, inda jami’anta ke binciken motar da aka kama a kan titin Lagos zuwa Badagry.

An gano cikin motar akwai kwanso guda shida na ma’adani mai launin azurfa mai ɗauke da guba mai ƙarfi da aka fi sani da corrosive mercury — wanda ake kyautata zaton ana amfani da shi wajen haɗa abubuwan fashewa.

Shugaban Kwastam na yankin, Kwanturola Ben Oramalugu, ya ce an kama mutum ɗaya da ake zargin yana da alaƙa da motar.

Ya bayyana cewa nasarar kama motar na nuna yadda Kwastam ke cikin shiri da kulawa wajen kare tsaron kasa.

Oramalugu ya kara da cewa wannan aiki na cikin matakan da Kwastam ke dauka don dakile ayyukan fasa-kwauri da sauran laifuka a iyakokin Najeriya.

Baya ga motar da ake zargin tana ɗauke da kayan haɗa bam, hukumar ta kuma kama wasu kayayyaki da dama da suka saɓa wa doka.

Kayayyakin sun hada da kuɗaɗen ƙasashen waje daga Birtaniya da Kanada, da Amurka da darajarsu ta kai kusan naira miliyan tara, wanda hakan ya saɓa dokar harajin kaya na waje.

Sauran kayayyakin da aka kama sun hada da robar ganyen wiwi guda 553 da buhunan shinkafar waje 1,415 da jarkokin man fetur guda 750, da kuma magungunan da ba a yi rijistarsu ba.

Kwanturola Oramalugu ya ce hukumar za ta miƙa kayayyakin da aka kama ga hukumomin da suka dace domin gudanar da bincike tare da ɗaukar mataki, da gurfanar da wadanda ake zargi.

daily post newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp