fidelitybank

Kwastam ta kama Kwantaina 20 na lalatattun Tumatir a Legas

Date:

Hukumar kwastam a Najeriya ta ce, ta kama duro 1,600 na tumatir ɗin da ya lalace wanda aka sanya cikin wasu kwantenoni guda 20 a jihar Legas.

An kama kwantenonin ne a tashar jiragen ruwan Legas, tare kuma da cafke wani mutum guda da ake zargi da shigo da su.

A cewar shugaban hukumar ta kwastam, Adewale Bashir, ya ce ana zargin kwantenonin mallakin wani kamfani ne mai suna Nikecristy Investment Limited.

Ya ce jami’ansu ne da ke sintiri ne suka samu nasarar kama kwantenonin guda 20, waɗanda daga bisani aka gano cewa suna ɗauke da tumatirin da ya lalace, wnada kuma zai yi wa mutane illa idan suka yi amfani da shi.

Ya ƙara da cewa kwantenonin da aka shigo da su daga ƙasar Sifaniya, za a biya musu kuɗin fito naira miliyan 116.2

“Abin Alla-wadai ne yadda waɗannan mutanen suka shigo da waɗannan kayayyaki da suka lalace zuwa cikin kasuwannin Najeriya,” in ji Adewale.

Ya ce zuwa yanzu kwantenonin na karkashin kulawarsu har sai bayan an kammala bincike.

hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp