fidelitybank

Kwastam ta ceto ‘yar shekara 17 dake kokarin ketarewa zuwa Libya

Date:

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS) ta ceto wata yarinya daga jihar Oyo.

An ceto yarinyar mai shekaru 17 a ranar 26 ga watan Nuwamba a birnin Kebbi a lokacin da ake zargin ta dauki hanyarta ta zuwa kasar Libya.

Tana tafiya ita kadai a inda aka kama ta, a wani wuri a karamar hukumar Yauri.

Kwanturolan hukumar NIS a Kebbi, Rabi Bashir-Nuhu ta shaida wa manema labarai cewa yarinyar ta yi ikirarin tafiya Sakkwato ne.

“Muna da yakinin cewa ana safarar ta ne don zuwa Libya domin a yi amfani da ita wajen yin aikin kwadago, karuwanci ko kuma girbin gabobi”, kamar yadda NAN ta ruwaito.

Matashiyar ta shaida wa jami’an shige da fice cewa mahaifiyarta ta aike ta domin ta gana da wata Zainab a Sakkwato.

Amma matar ta yi ikirarin cewa ba ta da lafiya lokacin da aka gayyace ta ofishin NIS da ke Kebbi.

“Wannan ya sa muka yi imanin cewa yarinyar ta kasance cikin fataucinsu. Ba ta da takarda ko da ko kwabo,” Bashir-Nuhu ya kara da cewa.

Kwamandan hukumar hana safarar mutane ta kasa (NAPTIP), Misbahu Iyya-Kaura, wanda ya tarbi yarinyar ya ce za a binciki lamarin.

hausa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp