Hukumar Kwastam ta kasa NCS a wani atisayen kan iyaka ta sake bindige wasu mutane biyu, bisa yunkurin kawo musu cikas a aikinsu a karamar hukumar Ringim ta jihar Jigawa.
Kakakin rundunar ‘yan sandan DSP Lawan Shiisu Adam ya tabbatar wa DAILY POST faruwar lamarin.
Ya ce lamarin ya faru ne da yammacin ranar Asabar a kauyen Gidan Lage yayin da wasu fusatattun matasa suka yi yunkurin hana rundunar hadin guiwa da jami’an tsaron kan iyaka gudanar da aikin a yankin.
Ya ce a yayin gudanar da ayyukan an kwato buhunan shinkafar kasashen waje da dama.
Shiisu ya bayyana cewa matasan kauyen sun taru sun yi yunkurin hana jami’an gudanar da aikin.
Ya bayyana cewa a sakamakon haka jami’an sun harba wasu harsasai kan masu zanga-zangar kuma an harbe mutane biyu kuma suka samu raunuka.
Shiisu ya ce ‘yan sanda sun garzaya wurin da laifin ya faru inda suka kai wadanda abin ya shafa asibitin Gabasawa da ke jihar Kano domin kula da lafiyarsu.
Wannan na zuwa ne kwanaki bayan da jami’an kwastam da ke aikin atisayen kan iyaka a kan iyakar Nijar da Najeriya sun haddasa fashewar motar dakob iskar gas da ta lalata gidaje, da shaguna da raunata da dama a karamar hukumar Babura.