fidelitybank

Kwastam sun harbe mutum biyu a Jigawa

Date:

Hukumar Kwastam ta kasa NCS a wani atisayen kan iyaka ta sake bindige wasu mutane biyu, bisa yunkurin kawo musu cikas a aikinsu a karamar hukumar Ringim ta jihar Jigawa.

Kakakin rundunar ‘yan sandan DSP Lawan Shiisu Adam ya tabbatar wa DAILY POST faruwar lamarin.

Ya ce lamarin ya faru ne da yammacin ranar Asabar a kauyen Gidan Lage yayin da wasu fusatattun matasa suka yi yunkurin hana rundunar hadin guiwa da jami’an tsaron kan iyaka gudanar da aikin a yankin.

Ya ce a yayin gudanar da ayyukan an kwato buhunan shinkafar kasashen waje da dama.

Shiisu ya bayyana cewa matasan kauyen sun taru sun yi yunkurin hana jami’an gudanar da aikin.

Ya bayyana cewa a sakamakon haka jami’an sun harba wasu harsasai kan masu zanga-zangar kuma an harbe mutane biyu kuma suka samu raunuka.

Shiisu ya ce ‘yan sanda sun garzaya wurin da laifin ya faru inda suka kai wadanda abin ya shafa asibitin Gabasawa da ke jihar Kano domin kula da lafiyarsu.

Wannan na zuwa ne kwanaki bayan da jami’an kwastam da ke aikin atisayen kan iyaka a kan iyakar Nijar da Najeriya sun haddasa fashewar motar dakob iskar gas da ta lalata gidaje, da shaguna da raunata da dama a karamar hukumar Babura.

daily post nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp