fidelitybank

Kwararan hujojin da ya sa Tinubu ya sutale Ministocinsa – Onanuga

Date:

Mai magana da yawun shugaban Najeriya, Bayo Onanuga, ya bayyana cewa sallamar ministoci da shugaban nasa ya yi ya dogara ne ga irin kallon da yadda ƴan Najeriya ke yi wa ministocin.

A wata hira da gidan talbijin na ARISE TV, Onanuga ya ce Tinubu ya yi amfani da tunanin ƴan Najeriya ne.

“A lokacin da aka rantsar da ministocin, shugaban lallai ya shaida musu cewa yana ƙarfin ikon ɗauka da sallamar mutum aiki kuma ba zai yi ƙasa a gwiwa ba wajen ganin ya kori duk wani ministan da ya fahimci ba ya aikin da ya kamata.”

“An yi wani taro a watan Oktoban bara inda shugaba Tinubu ya nanata maganarsa cewa a koyaushe zai iya sallamar duk wanda ya ga ba ya yn aiki.”

Onanuga ya ƙara da cewa sallamar ministocin ba lallai na nufin cewa ba su yi abin da shugaba Tinubun yake tsammani daga gare su ba.

“Shugaba Tinubu ya yi amfani da abin da ƴan Najeriya ke tsammani daga wurinsu. Makonnin da suka gabata a lokacin taron majalisar zartarwa, Shugaban ya ƙalubalanci ministocin su je su shaida wa ƴan Najeriya abin da suka yi a tsawon shekara guda.”

Shugaba Tinubu dai ya fahimci cewa ƴan Najeriya ba su gamsu da riƙon ludayin da dama daga ministocinsa amma kuma yana da ƙwarin gwiwar cewa gwamnati na yin bakin ƙaƙarinta amma ministocin ba sa fitowa su shaida wa al’ummar ƙasa abin da gwamnatin ke yi.” In ji Onanuga.

A ranar Laraba ne dai shugaba Tinubu ya sanar da yin garambawul ga ministoci da ma’aikatun gwamnatinsa, inda ya sallami ministocin guda biyar sannan ya sake wa mutum 10 ma’aikatu tare da naɗa sabbi guda bakwai.

mmm.nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp