fidelitybank

Kwansitabulare suna zubar da mutuncin mu – ‘Yan Sanda

Date:

Hukumar kula da aikin ‘yan sanda a Najeriya, ta koka kan abin da ta kira rashin nuna ƙwarewa da ƴan sandan sarauniya ko kuma ‘yan sandan sa-kai ke nunawa, a ƙoƙarin da suke yi wajen tallafa wa tsaron al’umma.

Hukumar ta bayyana haka ne cikin wata sanarwar da shugaban yaɗa labaranta, Ikechukwu Ani ya fitar, inda ta nemi a canza wa ‘yan sandan sarauniya kaki ko inifom, ko kuma a rushe ayyukansu a jihohi matuƙar ba za a riƙa biyan su haƙƙoƙin aiki da kuma kula da su ba.

A cewar hukumar, akwai hatsari a bai wa ‘yan sandan sarauniya bindiga, kuma a ba su lasisin samar da tsaro da tabbatar da doka da oda a jihohi da yankunan ƙasar, ba tare da biyan su albashi ba.

Hukumar ta gano cewa ‘yan sandan sarauniya suna karɓar cin hanci a hannun ƴan Najeriya ta hanyar tilastawa da kuma tsoratarwa.

Ta kuma ce hankalinta bai kwanta ba da tsarin rundunar ‘yan sandan sarauniya ta musamman da kuma yadda take tafiyar da ayyukanta a faɗin Najeriya.

Ta ce tuni ta tuntuɓi babban sufeton ƴan sandan Najeriya game da buƙatar sauya fasalin rundunar da kuma ayyukanta.

A cewar hukumar, sauya musu kaki, zai taimaka sosai wajen sa ido kan ayyukansu, da ma sauran jami’an ƴan sanda tare da tsame rundunar ƴan sandan Najeriya daga zargin da take sha saboda rashin ɗa’ar ‘yan sandan sarauniya.

An ruwaito Shugaban hukumar ta PSC, Solomon Arase wanda tsohon jami’in ɗan sanda ne yana cewa hukumarsa za ta yi aiki tare da shugabancin rundunar ƴan sanda ta ƙasar domin tsaftace ayyukan ‘yan sandan sarauniya.

legit nig. news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp