Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar New Nigeria People’s Party, NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya zabi Fasto Bishop Isaac Idahosa a matsayin matamakinsa a zaben 2023.
Jam’iyyar NNPP ta sanar da wannan labarin a shafinta na Tuwita ranar Alhamis.
Fasto Bishop Idahosa dan asalin Jihar Edo ne da ke Kudu maso Kudancin Najeriya.
Dan takarar mataimakin shugaban kasar na NNPP Bishop kuma babban fasto na Cocin God First Ministry, wadda aka fi sani da Illumination Assembly, Lekki Light Centre (LLC) a birnin Lagos.