Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP), Sanata Rabi’u Kwankwaso, ya yi watsi da ra’ayin cewa zai yi tunanin janyewa daga takarar shugaban kasa, domin marawa Peter Obi, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour.
Kwankwaso ya bayyana haka ne a ranar Laraba, yayin wata ganawa da manema labarai, a gidan Chatham House, dake birnin Landan.
Da yake amsa tambayar da wani dan kallo ya yi kamanceceniya da shirin yakin neman zaben NNPP da LP, tsohon gwamnan jihar Kano ya bayyana cewa magabatansa sun fi takwaransa na LP.
Kwankwaso ya ci gaba da cewa jam’iyyar NNPP ta samu goyon bayan al’umma sosai kuma za ta yi nasarar samun kuri’u musamman daga yankin Arewacin kasar nan tare da yin kutsawa a hankali a Kudu.
Ya ce, “Muna son kasa daya ce ta gadona; kasar da ake baiwa kowa dama bisa ga abinda ya kunsa maimakon addini ko kabila.