A karshen makon nan ne jami’ar jihar Kaduna wanda aka fi sani da KASU, ta rasa kwararren malamin ta, Farfesa Aminu Yusuf Usman.
Rabiu Musa Kwankwaso mai neman takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP, ya na cikin wadanda mutuwar Farfesa Aminu Yusuf Usman ta taba.
A wata sanarwa da ya fitar a yammacin Lahadi, 22 ga watan Junairu 2023, Rabiu Musa Kwankwaso ya yi jimamin mutuwar shehin malamin.
Da yake magana a dandalin Twitter, Sanata Kwankwaso ya shaidawa cewa malamin jami’ar yana cikin ‘yan kwamitin yakin neman takarar da yake yi.