fidelitybank

Kwankwaso ya caccaki gwamnatin Kano kan rikicin mutuwar mutanen Rimin Zakara

Date:

Wani jigon jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Musa Illiyasu Kwankwaso, ya caccaki shirin gwamnatin jihar Kano na kafa wani kwamiti da zai binciki kashe mutane hudu da aka yi a yayin wani atisayen rugujewa a Rimin Zakara da ke karamar hukumar Kumbotso a jihar.

A wata sanarwa da Kwankwaso ya fitar dauke da sa hannun sa da kan sa, ya yi kira ga Gwamna Abba Kabir Yusuf da kwamishinonin sa na filaye da ayyuka da su ziyarci iyalan wadanda abin ya shafa da kuma jajantawa.

Ya bayyana cewa irin wannan aiki kai tsaye ya zama wajibi domin a shawo kan rikicin, ya kuma bukaci gwamnati da ta biya iyalan wadanda suka mutu diyya tare da ware wa wadanda aka ruguza kadarorinsu na daban.

“Kingawar da gwamnati ta yi na ci gaba da gudanar da aikin rusau ba shi da amfani.

“Kafofin yada labarai da dama na cikin gida sun ruwaito cewa an ga jami’ai daga ma’aikatar kasa tare da jami’an tsaro a lokacin rugujewar,” in ji Kwankwaso.

Kwankwaso ya ci gaba da cewa, aikin rusau ya nuna rashin iya tafiyar da gwamnatinsa Gwamna Yusuf, inda ya ce shugaban jam’iyyar NNPP, Rabi’u Musa Kwankwaso ne ke yi masa magudi.

Ya yi gargadin cewa irin wadannan ayyuka za su iya jawo wa Gwamna Yusuf hasarar zaben 2027.

“Yanzu ya kamata mutanen Kano su gane su wane ne makiyansu. Babu abin da gwamnatin NNPP a Kano za ta kawo illa wahala, asarar rayuka, da barnata dukiyoyi, kamar yadda abin da ya faru a Rimin Zakara ke nan.” Inji shi.

Kwankwaso ya bayyana amincewa da shugabancin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, inda ya yaba da kokarinsa na magance talauci da yunwa a fadin kasar.

Jigon na APC ya kuma yabawa Amnesty International da suka yi Allah-wadai da kashe-kashen da aka yi a garin Rimin Zakara.

Ya ce: “Ina tsayawa tare da Amnesty International wajen yin Allah wadai da hare-haren da gwamnatin jihar Kano ke kai wa al’umma marasa galihu, wadanda ake azabtar da su tsawon shekaru da dama na gazawar tsara birane. Abubuwan da ke cike da rudani da barazanar da jami’an tsaro ke yi na kona gidaje ya sanya tsoro da firgici.

“Yin amfani da karfi mai kisa don mayar da matalauta marasa matsuguni wani mummunan zalunci ne. Dole ne a kawo karshen tashin hankalin da ake yi wa marasa galihu.”

Kwankwaso ya bukaci gwamnatin jihar da ta bi tsarin tsare-tsare na gari tare da mutunta jama’a, tare da tabbatar da kare hakki da rayukan mazauna yankunan.

daily post today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar Ĉ´ansandan jihar Kaduna, sun buĈ™aci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi Ĉ™ungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban Ĉ™aramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp