fidelitybank

Kwankwaso da tawagarsa ba za ta hana mu lashe zaben 2025 – APC

Date:

Jam’iyyar APC ta maida martani ga dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, Sanata Rabiu Kwankwaso.

Kwankwaso ya karbi wasu ‘yan siyasa da suka sauya sheka a gidansa ranar Laraba. A lokacin taron, ya bayyana cewa NNPP ta zama jam’iyya mai karfi da za ta rage tasirin APC a jihar Kano.

Ya ce: “Yanzu lokaci ya yi da za mu rage tasirin APC. Za mu yi aiki tukuru don ganin kuri’unsu sun ragu zuwa kasa da 15,000 a Kano kafin 2027.”

Ya kara da jan hankalin magoya bayansa su kasance masu jajircewa wajen tabbatar da nasarar jam’iyyar a zabukan gaba.

Amma a martaninsu, Daraktan Yada Labarai na APC, Alhaji Bala Ibrahim, ya bayyana cewa Kwankwaso da tawagarsa ba su da wani tasiri da zai zama barazana ga damar nasarar APC. Ya ce manyan jiga-jigan APC, ciki har da shugaban jam’iyyar na kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, za su tabbatar da nasarar jam’iyyar.

Jam’iyyar ta kara da cewa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu na daukar matakan da za su kara masa farin jini a wurin mutanen Kano kafin zaben 2027.

“Amma Kwankwaso ya manta cewa shugaban jam’iyyar mai mulki daga Kano yake ba, kuma ya taba zama gwamna mai karfi. Shi ne gwamna na karshe kafin wanda ke kan kujera a yanzu. Saboda haka yana da magoya baya.

“Shugaban kasa yana yin abubuwan da za su kara masa farin jini a Kano kafin 2027. Don haka Kwankwaso ba ya cewa zai ci zabe; yana cewa zai dauki wasu kuri’unmu, wanda ke nufin ya san kuri’u duka za su kasance na mu, amma zai dauki kadan, wanda ba zai kawo tangarda ga nasararmu ba.”

APC ta bayyana Kwankwaso a matsayin “’dan gudun hijirar siyasa” wanda ya zabi riko da Gwamna Abba Kabir Yusuf tamkar kyankyasai, yana yin kokarin banza na dawo da tasirinsa a harkokin siyasa a kasar.

vanguard 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp