fidelitybank

Kwankwaso da tawagarsa ba za ta hana mu lashe zaben 2025 – APC

Date:

Jam’iyyar APC ta maida martani ga dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, Sanata Rabiu Kwankwaso.

Kwankwaso ya karbi wasu ‘yan siyasa da suka sauya sheka a gidansa ranar Laraba. A lokacin taron, ya bayyana cewa NNPP ta zama jam’iyya mai karfi da za ta rage tasirin APC a jihar Kano.

Ya ce: “Yanzu lokaci ya yi da za mu rage tasirin APC. Za mu yi aiki tukuru don ganin kuri’unsu sun ragu zuwa kasa da 15,000 a Kano kafin 2027.”

Ya kara da jan hankalin magoya bayansa su kasance masu jajircewa wajen tabbatar da nasarar jam’iyyar a zabukan gaba.

Amma a martaninsu, Daraktan Yada Labarai na APC, Alhaji Bala Ibrahim, ya bayyana cewa Kwankwaso da tawagarsa ba su da wani tasiri da zai zama barazana ga damar nasarar APC. Ya ce manyan jiga-jigan APC, ciki har da shugaban jam’iyyar na kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, za su tabbatar da nasarar jam’iyyar.

Jam’iyyar ta kara da cewa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu na daukar matakan da za su kara masa farin jini a wurin mutanen Kano kafin zaben 2027.

“Amma Kwankwaso ya manta cewa shugaban jam’iyyar mai mulki daga Kano yake ba, kuma ya taba zama gwamna mai karfi. Shi ne gwamna na karshe kafin wanda ke kan kujera a yanzu. Saboda haka yana da magoya baya.

“Shugaban kasa yana yin abubuwan da za su kara masa farin jini a Kano kafin 2027. Don haka Kwankwaso ba ya cewa zai ci zabe; yana cewa zai dauki wasu kuri’unmu, wanda ke nufin ya san kuri’u duka za su kasance na mu, amma zai dauki kadan, wanda ba zai kawo tangarda ga nasararmu ba.”

APC ta bayyana Kwankwaso a matsayin “’dan gudun hijirar siyasa” wanda ya zabi riko da Gwamna Abba Kabir Yusuf tamkar kyankyasai, yana yin kokarin banza na dawo da tasirinsa a harkokin siyasa a kasar.

nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp