Yau Litinin kwana biyar kenan da ake fama da rashin wuta a wasu sassan babban birnin tarayyar Najeriya, Abuja.
A wata sanarwa da kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja AEDC, ya fitar a yau Litinin, ya bayar da hakuri kan rashin dawo da wutar wacce ta lalace tun ranar Alhamis din da ta wuce.
“Ba mu ji daÉ—in rashin dawo da wutar a kan lokaci kamar yadda muka ce tun farko ba. Amma muna aiki ka’in da na’in don tabbatar da gyara ta,” in ji sanarwar a cewar BBC.
Tun da fari dai wutar ta lalace ne sakamakon wata fashewa da aka samu a wata ƙaramar tashar wutar lantarkin da ke unguwar Katampe a babban birnin.
Kuma a sanarwar da ta fitar tun lokacin AEDC ya ce “wata fashewa da ta jawo tashin wuta ce ta lalata wutar da wasu unguwannin ke samu.”
Yankunan da rashin wutar ya shafa sun haɗa da Ƙwaryar cikin birnin Abuja da Katampe da Suleja da Gwagwalada da kuma Mpape.