Kwamitin yaƙin neman zaben Donald Trump ya shigar da ƙara kan jam’iyyar Labour da ke mulki a Birtaniya, inda ya zarge ta da yin katsalandan a zaɓen Amurka.
Sanarwar da ofishin yaƙin neman zaɓen jam’iyyar Republican ya fitar ta yi nuni da rahoton da wata jaridar Birtaniya (The Telegraph) ta bayar cewa wasu mutane da ke da alaka da jam’iyyar Labour sun je Amurka don yaƙin neman zabe a madadin ƴar takarar jam’iyyar Democrat, Kamala Harris.
Bayanai na nuna cewa har yanzu babu wani martani a hukumance daga Jam’iyyar Labour, amma jami’an jam’iyyar sun ce waɗanda suka yi tafiyar ba jam’iyyar labour ce ta ɗauki nauyinsu ba.