Kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya zai gudanar da taron gaggawa a yau Litinn domin tattauna batun faduwar gwamnatin shugaba Bashar al Assad na Syria, biyo bayan hare-haren ba za ta daga ‘yan tawaye masu kishin Islama.
Rasha ce ta bukaci a gudanar da wannan taro, wato aminiyar shugaban da aka hambarar.
Wannan na zuwa ne bayan kafar yada labarai a Moscow ta tabbatar da cewa Assad da iyalansa sun samu mafakar siyasa a kasar.
Amurka ce ke kan gaba wajen martani a game da hambarar da gwamnatin Assad, inda shugaba Biden ya ce faduwar gwamnatin Assad wani muhimmanci na adalci bayan shafe shekaru aru-aru na mulkin danniya, sai dai ya yi gargadin cewa kasancewar ‘yan tawaye ne suka kwace kasar akwai sauran barazana da rashin tabbas.
Ya ce za su yi aiki da dukkanin kungiyoyin kasar har da Majalisar Dinkin Duniya wajen tabbatar da zaman lafiya.
Mista Biden ya kuma gargadi kungiyar ‘yan tawayen da kada tayi amfani da wannan dama wajen haifar da sabon rikici a gwamnatin riko.