Majalisar wakila ta kasa, ta umarci kwamitinta mai kula da hukumar gidajen gyaran hali da ya gudanar da bincike kan yanayin da ake tsare mutane a Najeriya.
Shugaban marasa rinjaye a majalisar ne ya gabatar da wata buƙatar gaggawa, inda ya nuna damuwa kan mummunan yanayin da ma’aikatan gidajen yari ke aiki, da kuma halin ƙunci da fursunoni ke ciki.
Honarabul Kabiru Alhassan Rurum ya shaidawa BBC cewa na dauki matakin ne domin yin gyara a harkokin da suka shafi gidajen kason, duba da yadda suke cunkushewa da marasa laifi.
Ya kuma Kce akwai abin takaci ganin yadda ake cika fursunoni a daki guda, inda mutum 10 ya kamata su kwana sai ka an samu sama da mutum 50 a ciki.