Kwamitin tattaunawa da samar da matsaya kan mafi ƙanƙantar albashi zai gana da wakilan manyan ƙungiyoyin ƙwadago NLC da TUC, a gobe Talata da safe.
Taron zai kasance na takwas kenan tun bayan da gwamnatin Najeriya ta kafa kwamitin domin cimma daidaito kan mafi ƙankantar albashi a ƙasar.
Za a yi taron ne yayin da ƙungiyoyin ƙwadago na NLC da TUC suka fara yajin aiki na sai-baba-ta-gani a faɗin Najeriya a yau Litinin saboda ƙin yarda da gwamnati ta yi da matsayar ƙungiyoyin kan albashi mafi ƙanƙanta.
Jaridar Guardian ta ruwaito cewa, kwamitin ya gayyaci wakilan manyan ƙungiyoyin ƙwadagon ne domin zaman tattaunawa a gobe Talata 4 ga watan Yuni a otal ɗin Nicon Luxury, da ke Abuja, da ƙarfe 10 na safe.
Sanarwar ta ƙara da cewa ga manyan masu ruwa da tsaki a tattaunawar da ƙila sun tafi taron ƙungiyar ƙwadago ta duniya da ake yi a Switzerland, Sakataren Kwamitin, Ekpo Nta ya ce an tanadi manhajar Zoom domin halartarsu tattaunawar ta intanet.