fidelitybank

Kwamiti ya gayyaci kungiyoyin kwadago a kan tsunduma yajin aiki

Date:

Kwamitin tattaunawa da samar da matsaya kan mafi ƙanƙantar albashi zai gana da wakilan manyan ƙungiyoyin ƙwadago NLC da TUC, a gobe Talata da safe.

Taron zai kasance na takwas kenan tun bayan da gwamnatin Najeriya ta kafa kwamitin domin cimma daidaito kan mafi ƙankantar albashi a ƙasar.

Za a yi taron ne yayin da ƙungiyoyin ƙwadago na NLC da TUC suka fara yajin aiki na sai-baba-ta-gani a faɗin Najeriya a yau Litinin saboda ƙin yarda da gwamnati ta yi da matsayar ƙungiyoyin kan albashi mafi ƙanƙanta.

Jaridar Guardian ta ruwaito cewa, kwamitin ya gayyaci wakilan manyan ƙungiyoyin ƙwadagon ne domin zaman tattaunawa a gobe Talata 4 ga watan Yuni a otal ɗin Nicon Luxury, da ke Abuja, da ƙarfe 10 na safe.

Sanarwar ta ƙara da cewa ga manyan masu ruwa da tsaki a tattaunawar da ƙila sun tafi taron ƙungiyar ƙwadago ta duniya da ake yi a Switzerland, Sakataren Kwamitin, Ekpo Nta ya ce an tanadi manhajar Zoom domin halartarsu tattaunawar ta intanet.

latest news nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp