Kwamishinan ilimi na jihar Kano, Sanusi Said Kiru, ya mika takardar murabus dinsa a ranar Lahadi.
PlatinumPost ta rawaito cewa, a ranar Asabar ne Ganduje ya bayar da wa’adin sa’o’i arba’in da takwas ga duk masu rike da mukaman siyasa masu neman mukamai da su yi murabus.
Sai dai a wata sanarwa da ya sanyawa hannu a ranar Lahadi, Kiru ya ce, ya mika takardar murabus din ne bisa bin umarnin Gwamna Ganduje.
A cewarsa, ya kuma yi murabus ne, domin ya tsaya takarar dan majalisar wakilai ta tarayya mai wakiltar mazabar Kiru/Bebeji, a karkashin jam’iyyar, APC mai zuwa 2023.
Kwamishinan ilimi na jihar Kano, Sanusi Said Kiru ya mika takardar murabus dinsa a ranar Lahadi.
PlatinumPost ta rahoto cewa a ranar Asabar ne Ganduje ya bayar da wa’adin sa’o’i arba’in da takwas ga duk masu rike da mukaman siyasa masu neman mukamai da su yi murabus.
Sai dai a wata sanarwa da ya sanyawa hannu a ranar Lahadi, Mista Kiru ya ce ya mika takardar murabus din ne bisa bin umarnin Gwamna Ganduje.
A cewarsa, ya kuma yi murabus ne domin ya tsaya takarar dan majalisar wakilai ta tarayya mai wakiltar mazabar Kiru/Bebeji, a karkashin jam’iyyar All Progressives Congress, APC mai zuwa 2023.