Kwamishinan kananan hukumomi da masarautu na jihar Ogun, Afolabi Afuape, ya shawarci gwamnatin tarayya da ta sake duba shirin masu yi wa kasa hidima (NYSC).
Afuape ya ce, hakan ya zama dole domin magance karuwar rashin aikin yi a kasar.
Kwamishinan ya bayyana hakan ne a lokacin da yake mayar da martani kan korafe-korafen da shugaban kungiyar musulmin jihar ya nuna masa.
Gwamnatin mulkin soja karkashin Janar Yakubu Gowon (rtd) ce, ta kafa tsarin NYSC jim kadan bayan yakin basasa domin a samu saukin hadewa.
Amma, Afuape yayin da yake jawabi ga kungiyar, ya ba da shawarar sake duba aikin yi wa kasa hidima na shekara guda.