fidelitybank

Kwalejin Kimiya da Fasaha a Kano ta kori ɗalibai

Date:

Kwalejin Kimiyya da Fasahar lafiya ta Aminu Dabo dake Kano ta kori dalibai 12, bisa samun su da laifin satar amsa a lokacin da suke rubuta jarabawa.

Wata sanarwa da shugaban sashen hulda da jama’a na kwaleji, Abdullahi Usman ya fitar a ranar Talata, ta ce an kama wasu dalibai 13 (‘yan aji 2) bisa laifuka daban-daban da suka shafi rashin da’a a yayin gudanar da jarrabawa a makarantar.

Sanarwar ta ce an kama  daliban suna tafka magudin jarrabawa da rashin da’a wanda ya saba wa ka’idojin Kwalejin a lokacin jarrabawar zango na biyu na shekarar 2021/2022.

Sanarwar ta ce, ”Hukumar Kwalejin ta dauki mataki  kan daliban ne, Saboda abin da  su ka yi ya saba da dokar makarantar, inda a ka yi amfani da shawarwarin da kwamitin ladabtarwa ya bayar.

Rahotanni sun nuna cewa, daliban da abin ya shafa an kama su da hannu dumu-dumu cikin rashin da’a da kuma wasu abubuwa da suka saba wa tsarin kwalejin a lokacin jarrabawar.

Hukumar gudanarwar, ta umurci sauran daliban da aka wanke da su koma kwalejin a ranar Litinin, 17 ga watan Janairu, 2022, domin ci gaba da jarrabawa tare da gargaɗin sauran ɗaliban.

the nation newspaper nigeria today latest

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...

Ba za mu jingine yajin aiki ba har sai an biya mana buƙatun mu – Ma’aikatan Jinya

Shugaban ƙungiyar ma'aikatan jinya ta Najeriya, Morakinyo-Olajide Rilwan ya...

Za a fara yi wa Dalibai gwajin kwaya kafin su shiga jami’a – NDLEA

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta fara yi wa...

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...
X whatsapp