fidelitybank

Kwalejin Kimiya da Fasaha a Kano ta kori ɗalibai

Date:

Kwalejin Kimiyya da Fasahar lafiya ta Aminu Dabo dake Kano ta kori dalibai 12, bisa samun su da laifin satar amsa a lokacin da suke rubuta jarabawa.

Wata sanarwa da shugaban sashen hulda da jama’a na kwaleji, Abdullahi Usman ya fitar a ranar Talata, ta ce an kama wasu dalibai 13 (‘yan aji 2) bisa laifuka daban-daban da suka shafi rashin da’a a yayin gudanar da jarrabawa a makarantar.

Sanarwar ta ce an kama  daliban suna tafka magudin jarrabawa da rashin da’a wanda ya saba wa ka’idojin Kwalejin a lokacin jarrabawar zango na biyu na shekarar 2021/2022.

Sanarwar ta ce, ”Hukumar Kwalejin ta dauki mataki  kan daliban ne, Saboda abin da  su ka yi ya saba da dokar makarantar, inda a ka yi amfani da shawarwarin da kwamitin ladabtarwa ya bayar.

Rahotanni sun nuna cewa, daliban da abin ya shafa an kama su da hannu dumu-dumu cikin rashin da’a da kuma wasu abubuwa da suka saba wa tsarin kwalejin a lokacin jarrabawar.

Hukumar gudanarwar, ta umurci sauran daliban da aka wanke da su koma kwalejin a ranar Litinin, 17 ga watan Janairu, 2022, domin ci gaba da jarrabawa tare da gargaɗin sauran ɗaliban.

mmm.nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp