fidelitybank

Kwalejin Kimiya da Fasaha a Kano ta kori ɗalibai

Date:

Kwalejin Kimiyya da Fasahar lafiya ta Aminu Dabo dake Kano ta kori dalibai 12, bisa samun su da laifin satar amsa a lokacin da suke rubuta jarabawa.

Wata sanarwa da shugaban sashen hulda da jama’a na kwaleji, Abdullahi Usman ya fitar a ranar Talata, ta ce an kama wasu dalibai 13 (‘yan aji 2) bisa laifuka daban-daban da suka shafi rashin da’a a yayin gudanar da jarrabawa a makarantar.

Sanarwar ta ce an kama  daliban suna tafka magudin jarrabawa da rashin da’a wanda ya saba wa ka’idojin Kwalejin a lokacin jarrabawar zango na biyu na shekarar 2021/2022.

Sanarwar ta ce, ”Hukumar Kwalejin ta dauki mataki  kan daliban ne, Saboda abin da  su ka yi ya saba da dokar makarantar, inda a ka yi amfani da shawarwarin da kwamitin ladabtarwa ya bayar.

Rahotanni sun nuna cewa, daliban da abin ya shafa an kama su da hannu dumu-dumu cikin rashin da’a da kuma wasu abubuwa da suka saba wa tsarin kwalejin a lokacin jarrabawar.

Hukumar gudanarwar, ta umurci sauran daliban da aka wanke da su koma kwalejin a ranar Litinin, 17 ga watan Janairu, 2022, domin ci gaba da jarrabawa tare da gargaɗin sauran ɗaliban.

spw

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp