Kwalejin Kimiyya da Fasahar lafiya ta Aminu Dabo dake Kano ta kori dalibai 12, bisa samun su da laifin satar amsa a lokacin da suke rubuta jarabawa.
Wata sanarwa da shugaban sashen hulda da jama’a na kwaleji, Abdullahi Usman ya fitar a ranar Talata, ta ce an kama wasu dalibai 13 (‘yan aji 2) bisa laifuka daban-daban da suka shafi rashin da’a a yayin gudanar da jarrabawa a makarantar.
Sanarwar ta ce an kama daliban suna tafka magudin jarrabawa da rashin da’a wanda ya saba wa ka’idojin Kwalejin a lokacin jarrabawar zango na biyu na shekarar 2021/2022.
Sanarwar ta ce, ”Hukumar Kwalejin ta dauki mataki kan daliban ne, Saboda abin da su ka yi ya saba da dokar makarantar, inda a ka yi amfani da shawarwarin da kwamitin ladabtarwa ya bayar.
Rahotanni sun nuna cewa, daliban da abin ya shafa an kama su da hannu dumu-dumu cikin rashin da’a da kuma wasu abubuwa da suka saba wa tsarin kwalejin a lokacin jarrabawar.
Hukumar gudanarwar, ta umurci sauran daliban da aka wanke da su koma kwalejin a ranar Litinin, 17 ga watan Janairu, 2022, domin ci gaba da jarrabawa tare da gargaɗin sauran ɗaliban.