Wasu mutum biyu sun rasu, sannan ana ci gaba da neman 13 bayan kifewar wani kwale-kwale a karamar hukumar Ijaw na jihar Bayelsa.
Lamarin ya faru ne a yammacin ranar Talata bayan da jirgin ruwan É—auke da fasinjoji ya garu da wani na mai kamun kifi.
Wani shaida ya bayyana wa Jaridar Daily Trust cewa ana can ana aiki domin ceto sauran fasinjoji da suka ɓata.
Shugaban Ć™ungiyar ma’aikatan kula da tashar jiragen ruwa a jihar Bayelsa, Comrade Ogoniba Ipigansi, ya tabbatar da faruwar lamarin – inda ya ce ba a ga fasinjoji 13 ba zuwa yanzu.
Comrade Ipigansi ya ce ƙungiyar ya ce sun samu labari jim kaɗan bayan faruwar lamarin, amma rashin kyawun hanyoyi sadarwa ya janyo cikas ga aikin ceto a yankin.