fidelitybank

Kwale-Kwale ya kafe tare da mutuwar mutane 20 a Binuwai

Date:

Akalla mutane 20 ne aka ruwaito sun mutu bayan wani jirgin ruwa ya kife a kogin Benue a ranar Asabar.

Rahotanni na cewa kwale-kwalen nasu ya kife ne a lokacin da suke tsallakawa daga Ocholonya a karamar hukumar Agatu zuwa Odenyi a karamar hukumar Nasarawa Toto ta jihar Nasarawa bayan gudanar da ayyukansu a kasuwar Ocholonya.

Wani shaidan gani da ido, Fada Awatsu ya ce, “kwale-kwalen katako na cike da kaya da fasinjoji daga kasuwar Ocholonya.

“An yi lodi fiye da kima kuma jim kadan da tashinsa sai fasinjojin da ke cikin jirgin suka yi hayaniya kuma daga karshe ya fadi ya gangara cikin ruwa.”

Sun fito ne daga Agatu, Agbashi, Ajima, Okpata, Rukubi, Ondoli, Odadu a karamar hukumar Doma.

Majiyoyi sun ce wadanda abin ya shafa mata ne da kananan yara da ke dawowa gida daga kasuwa.

Ya zuwa yanzu dai an gano gawarwaki 19 daga hatsarin, yayin da ake ci gaba da aikin ceton wasu.

Da aka tuntubi shugaban karamar hukumar Agatu, Hon.Melvin Ejeh ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce, “wadanda aka kashen suna dawowa ne daga kasuwar Ocholonya zuwa kauyensu da ke kusa da jihar Nasarawa.

“Bishiyoyi a cikin kogin sun hana ganin ma’aikacin jirgin kuma lokacin da kwalekwalen ya bugi bishiyoyi, ya fado ya kife.”

Hon Ejeh ya ce an gano gawarwaki sama da 20 kuma ana ci gaba da aikin ceto.

Ya ce zai tura jami’an majalisar domin yi wa iyalan mamacin ta’aziyya.

sunnnewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar Æ´an Æ™asarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp