Akalla mutane 20 ne aka ruwaito sun mutu bayan wani jirgin ruwa ya kife a kogin Benue a ranar Asabar.
Rahotanni na cewa kwale-kwalen nasu ya kife ne a lokacin da suke tsallakawa daga Ocholonya a karamar hukumar Agatu zuwa Odenyi a karamar hukumar Nasarawa Toto ta jihar Nasarawa bayan gudanar da ayyukansu a kasuwar Ocholonya.
Wani shaidan gani da ido, Fada Awatsu ya ce, “kwale-kwalen katako na cike da kaya da fasinjoji daga kasuwar Ocholonya.
“An yi lodi fiye da kima kuma jim kadan da tashinsa sai fasinjojin da ke cikin jirgin suka yi hayaniya kuma daga karshe ya fadi ya gangara cikin ruwa.”
Sun fito ne daga Agatu, Agbashi, Ajima, Okpata, Rukubi, Ondoli, Odadu a karamar hukumar Doma.
Majiyoyi sun ce wadanda abin ya shafa mata ne da kananan yara da ke dawowa gida daga kasuwa.
Ya zuwa yanzu dai an gano gawarwaki 19 daga hatsarin, yayin da ake ci gaba da aikin ceton wasu.
Da aka tuntubi shugaban karamar hukumar Agatu, Hon.Melvin Ejeh ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya ce, “wadanda aka kashen suna dawowa ne daga kasuwar Ocholonya zuwa kauyensu da ke kusa da jihar Nasarawa.
“Bishiyoyi a cikin kogin sun hana ganin ma’aikacin jirgin kuma lokacin da kwalekwalen ya bugi bishiyoyi, ya fado ya kife.”
Hon Ejeh ya ce an gano gawarwaki sama da 20 kuma ana ci gaba da aikin ceto.
Ya ce zai tura jami’an majalisar domin yi wa iyalan mamacin ta’aziyya.