Aƙalla mutum 25 ne suka mutum aka kwantar da wasu da dama kuma a asibitoci sakamakon ɓarkewar cutar kwalara – amai da gudawa – a ƙananan hukumomi uku a jihar Sokoto.
Kwamishinar lafiya ta jihar Asabe Balarabe wadda ta bayyana haka ga manema labaraai a Sokoto, ta ce ana yi wa mutum 15 da suka kamu da cutar daga yankunan ƙaramar hukumar Sokoto ta Arewa da Silame da kuma Kware, magani.
Asabe ta kuma ce annobar ta kama mutum 1,160 ne kuma tuni 25 sun rasu a sakamakon cutar.
Kwamishinar wadda ta ce tuni an raba magunguna a ƙananan hukumomi 18 ta ce kwamitocin taimakon gaggawa na jihar na aiki tuƙuru tare da gwamnatin jiha domin dakatar da bazuwar cutar.