fidelitybank

Kwalara ta kashe mutane biyu a Katsina

Date:

Gwamnatin jihar Katsina ta tabbatar da mutuwar mutum biyu sakamakon kwalara da ta zama annoba a Najeriya.

Hukumomin lafiya na jihar sun ce sun dauki matakan gaggawa na dakile bazuwar cutar inda yanzu mutum 118 suka harbu a jihar.

Dr Bishir Gambo Saulawa, kwamishinan lafiya na jihar ta Katsina ya shaida wa BBC cewa cikin matakan da suka dauka shi ne na samar da magungunan da suka kamata a matakin kananan hukumomi har da sinadarin tsaftace ruwa da suka rarraba.

“Babban musabbabin kwalara shi ne ruwa, shi ne kuma ake kokari a rage.” in ji kwamshinan.

A cewarsa, kananan hukumomin da aka yi asarar rayukan sune Dutsinma da kuma Katsina. Ya bayyana cewa cutar ta fi kamari a karamar hukumar Kusada inda a wajen kadai aka samu mutum 62 da suka kamu da cutar ta amai da gudawa.

Kwamishinan ya ce babban aikin da ke gabansu a yanzu shi ne na dakile bazuwar cutar inda ya nuna cewa ana wayar da kan mutane game da muhimmancin tsaftace muhallansu domin kare kansu daga kamuwa da cutar ta amai da gudawa.

nigeria peace corps

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp