fidelitybank

Kwace yankunan Gaza da Isra’ila ke yi ya saɓa doka – Majalisar Ɗinkin Duniya

Date:

Ofishin kare hakkin bil adama na Majalisar Dinkin Duniya ya fada a ranar Talata cewa, Isra’ila ta fadada tare da karfafa matsuguni a yankin Yammacin Kogin Jordan da ta mamaye a matsayin wani bangare na ci gaba da shigar da yankunan kasar Isra’ila, wanda ya saba wa dokokin kasa da kasa.

An tattaro cewa rahoton, wanda za a gabatar da shi ga kwamitin kare hakkin bil adama na Majalisar Dinkin Duniya a karshen wannan wata, ya zo ne a daidai lokacin da ake kara samun fargabar sake hadewa, biyo bayan sauye-sauyen manufofin Amurka a karkashin Shugaba Donald Trump da kuma kafa sabbin matsuguni a yankunan yammacin kogin Jordan da ake gani a matsayin wani bangare na kasar Falasdinu a nan gaba.

Babban jami’in MDD Volker Turk ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya raka rahoton, inda ya bukaci kasashen duniya da su dauki matakai masu ma’ana a kan ci gaban da Isra’ila ke yi na samar da zaman lafiya.

“Masar da Isra’ila ta yi wa wasu sassan farar hula nata zuwa yankin da ta mamaye ya zama laifin yaki.

Ya ce: “Dole ne Isra’ila ta dakatar da dukkan ayyukan matsugunan nan da nan gaba daya, sannan ta kwashe dukkan matsugunan ta, ta dakatar da tura al’ummar Palasdinu tilas, sannan ta hana tare da ladabtar da hare-haren da jami’an tsaronta da matsugunanta ke kaiwa.”

Idan dai za a iya tunawa Isra’ila ta fice daga kwamitin kare hakkin bil’adama na Majalisar Dinkin Duniya a farkon wannan shekarar, inda ta yi zargin cewa tana nuna kyama ga Isra’ila.

A halin da ake ciki kuma rundunar sojin Isra’ila ta ce tana gudanar da ayyukan yaki da ta’addanci a yammacin gabar kogin Jordan tare da kai hari kan wasu da ake zargin ‘yan ta’adda ne.

bbc nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp