fidelitybank

Kuɗirin cire rigar kariya ga Gwamnoni ya tsallake karatu na biyu

Date:

Ƙudurin dokar da ke neman cire rigar kariya ga mataimakin shugaban ƙasa da gwamnoni da mataimakansu ya tsallake karatu na biyu, a majalisar wakilan Najeriya.

Ƙudurin na daga cikin gwamman ƙudurorin da majalisar ke aiki a kansu, a wani ɓangare na yin gyaran fuska ga kundin tsarin mulkin ƙasar na shekarar 1999.

Cikin abubuwan da ƙudirin ke fatan cimmawa idan ya zama doka zai kuma tabbatar da rigar kariya ga shugaban ƙasa.

Ƙudurin na fatan cire rigar kariya ga mataimakin shugaban ƙasa, gwamnoni da mataimakansu zai taimaka wajen magance matsalar cin hanci da rashawa, hana ɗaukar hukunci a kansu sakamakon wani laifi da suke aikatawa da ƙarfafa tsare gaskiya a tsakanin masu riƙe da muƙamin gwamnati.

Sai dai ƙudurorin dokar na buƙatar amincewar duka majalisun dokoki biyu, na wakilan da na dattawan kafin ya kai ga shugaban ƙasa, wanda zai rattaba hannu a kansa sannan ya zama doka.

daily post news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp