fidelitybank

Kuwait ta mikawa Indiya gawarwakin mutane 45 da gobara ta kona

Date:

Wani jirgin saman sojojin Indiya ya dawo da gawarwakin ma’aikatan Indiya 45 da suka mutu a wata mummunar gobara da ta tashi a Kuwait.

Gobarar ta tashi ne a ranar Laraba a wani gini da ke birnin Mangaf, inda ma’aikatan Indiya 176 suke.

Hukumomin Kuwaiti sun bayar da rahoton cewa gobarar ta lashe rayukan mutane 50 da suka hada da Indiyawa 45 da ’yan kasar Philippines uku, inda har yanzu ba a tantance mutane biyu da suka mutu ba.

A ranar alhamis, ministar Indiya Kirti Vardhan Singh ta isa Kuwait don taimakawa wajen gano waÉ—anda abin ya shafa da kuma saukaka komawa Indiya.

Singh ta ce ana gudanar da gwaje-gwajen DNA don tabbatar da asalin waÉ—anda suka mutu.

Kuwait, wacce ta dogara kacokan kan ayyukan baÆ™in haure, tana da kashi biyu bisa uku na al’ummarta da suka hada da ma’aikatan kasashen waje, musamman a bangaren gine-gine da na cikin gida.

Ƙungiyoyin kare haƙƙin bil’adama sun sha nuna damuwa game da yanayin rayuwar waÉ—annan ma’aikata.

Gobarar ta kuma raunata ma’aikata da dama waÉ—anda yawancinsu ‘yan Æ™asar Indiya ne.

Gwamnatin Indiya na haÉ—a kai domin bayar da tallafi da kuma dawo da waÉ—anda abin ya shafa zuwa kasarsu. In ji BBC.

nnn hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp