fidelitybank

Kutsawar da Ukraine ke yi cikin ƙasar mu akwai hannun NATO da ƙasashen Yamma – Rasha

Date:

Rasha ta ce akwai hannun ƙungiyar tsaro ta Nato da kuma ƙasashen yamma a kutsen da Ukraine ke yi cikin yankin Kursk na Rasha.

Cikin wata hira da wata jarida ta Izvestia ta yi da wani jami’in gwamnatin Rasha Nikolao Patrushev, ya ce suna ganin irin abubuwan da sojojin Ukraine ke yi a yankin Kursk, akwai hannun ƙasashen yamma da kuma ƙungiyar tsaro ta Nato a ciki. In ji BBC.

Ya ce,” Sanarwar da Amurka ta fitar cewa babu hannunta a irin kutsen da Ukraine ke yi a yankin Kursk, ba gaskiya bane, saboda idan har babu hannunsu babu yadda za a yi Ukraine ta rinka abin da ta ke a yanzu a yankunan Rasha.”

A farkon makonnan ne Amurka ta fitar da sanarwar cewa bata da masaniya a kan irin abubuwan da Ukraine ke yi kuma babu hannunta ko koɗan.”

Ukraine dai ta ce sojojinta na ci gaba da nausawa cikin yankunan Rasha har ma ta kafa wani ofis na sojojinta a Rasha.

Ta ce, ‘Za mu ci gaba da kafa ofisoshi ma a duk yankin da muka ƙwace’

A baya bayannan dai sojojin Ukraine suka kai wani harin bazata zuwa lardin Kursk na Rasha, da ke maƙwabtaka da ita. Sai dai an kasa samun sahihan bayanai kan wannan hari da aka kai kawo yanzu.

Tun da farko, an yi tsammanin cewa wasu ƙungiyoyi masu zagon ƙasa ga Rasha ne waɗanda ke adawa da gwamnatin shugaba Vladimir Putin suka kai harin.

Ukraine ta yi amfani da rashin isassun jami’an tsaro a kan iyaka wajen kutsawa zuwa cikin Rasha, a yayin da Rasha ta karkata aƙalar sojojinta zuwa wurare daban-daban da ake ci gaba da gwabza fada

the nation newspaper 
today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp