fidelitybank

Kuskure ne babba tsofaffin shugabanni su nuna ɗan takarar su – Kwankwaso

Date:

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP), Rabi’u Kwankwaso, ya yi ikirarin cewa, shugabannin siyasa na tafka kura-kurai wajen amincewa da ‘yan takara a fili gabanin zaben badi.

Kwankwaso ya bayyana haka ne a ranar Laraba a lokacin da ya ziyarci gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki, a gidan gwamnati dake Benin.

A kwanakin baya ne tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo da shugaban Ijaw na kasa, Edwin Clark, suka fito domin amincewa da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party (LP), Peter Obi.

A yanzu Kwankwaso ya ce, an amince da hakan ne bisa ra’ayin addini da kabilanci.

“Wasu daga cikin mutanen… mun ga labarai cewa suna goyon bayan Mista A ko Mista B, ina ganin kuskure ne babba. Waɗannan shugabanni ne da nake girmamawa. A rayuwarka akwai lokacin da ka zama dan siyasa na gaske, ba dan siyasa ba.

“Har ila yau, zan iya gaya muku cewa duk wani dan takara ko jam’iyyar da ta fito da fuskar kabilanci ko kuma batun addini, waccan jam’iyya, wannan dan takarar, ina mai tabbatarwa a matakin kasa, ta fadi zaben kafin a fara.

“Kuma ina so in ba shugabanninmu shawara: su daina tozarta kansu. Muna girmama su sosai,” inji Kwankwaso.

tribune news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...
X whatsapp